Zargin Sace Wayar Madagwal Da Madam Korede Tayi/G Fresh Ya Musanta Maganar Bashi Da Lapiya

Image
A Ranar Lahadi Babban Kaftin Na Nijeriya Ahmad Musa Ya Hada Wani Wasan Kwallon Kafar Na Manyan Sanannu A Arewa Domin Yin Zumunchi Inda Jaruma Da Manyan Celebrate Da Suka Hada Da Ali Nuhu, Umar M Sharif Madagwal ,Madam Korede Da Dai Sauransu Suka Halirchi Wajen PLAY ▶️ Saide A Yayin Da Aka Kammala Taron Ne Sai Wata Magana Ta Fito Ta Bakin Madagwal Inda Ya Bayyana Cewar Madam Korede Ta Sace Masa Waya A Yayin Da Suke Cin Abinchi Bayan Kammala Wasan Nasu Amma Nata Bangaren Madam Korede Ta Karya Batun Inda Ta Musanta Abun Har Abun Yakai Su Ga Zuwa Ofishin Yan Sanda Don Neman Hanginsa Da Yayi Kirarin Ta Tauye Masa Madagwal Ya Bayyana Hakane A Tattaunawa Sa Da  Freedom Radio Har Ya Bayyana Musu Yadda Abun Ya Faru Da Kuma Matsayar Kas Din Nasu Inda Yace Tun Fara Sun Sami Matsala Ne A Kwanakin Baya Da Madam Korede Inda Daga Bisani Ya Bashi Hakuri Har Allah Ya Kawo Wannan Taron Suka Hadu Da Ita Take Bibiyar PLAY ▶️ Yace A Lokacin Da Suka Kammala Wasan Shi Kuma Da Kaya...

Dalilin Da Yasa Na Daina Runguma da sumbuta a fim – Ali Nuhu

Fitattaccen jarumin Fina-finan Hausa da na kudu, Nollywood, Ali Nuhu ya shaida cewa dalilin da yasa ya daina sumbatar mata da runguma a fina-finan Najeriya shine fada da yayi wa kan sa ya daina yin hakan.

Ali ya kara da cewa a matsayin sa na musulmi dan Arewa mai cikakken tarbiyya, shi jakada ne na inda ya fito a ko ina ya ke. Hakan ya sa yayi karatun ta natsu don kiyaywe karantarwar Addinin sa, addinin musulunci da martaba al’umman sa.

“A shekarun baya idan ka lura na yi irin wadannan fina-finai amma daga baya da na ga korafe-korafen mutane, ka ga mutum jakada ne na Arewa…kuma Musulmi…shi ya sa ni yanzu ba na fitowa a irin wadannan fim din.”

Haka Ali Nuhu ya shaida wa BBC Hausa a yar gajeruwar hira da ta yi dashi.

Ali Nuhu ya fito a manyan shirye-shiryen kudu da dama, shirye shiryen da suka yi suna da fice a Duniya. Yana daga cikin fitattun jaruman da suka fara fitowa a fina-finan ‘yan kudu wato Nollywood daga Arewa kuma suka yi fice matuka.


Baya ga zama tauraro, Ali Nuhu ya zama baya goya marayu a farfajiyar Kannywood inda ya kyankyasa jarumai da dama da yanzu suke shanawa a harkar fim ciki akwai Jaruma Rahama Sadau, Nafeesat Abdullahi, Zaharadden Sani, Nuhu Abdullahi da dai Sauransu. Dukkan su dai Kamfanin FKD mallakar Ali Nuhu ne ta yi rainon su har suka girma.


Ali Nuhu yayi fina-finai da ba zai iya fadin yawan su kamar yadda ya fadi sannan kuma ya samu kyaututtuka da lambar yabo masu yawa a gida da wajen Najeriya.

Comments

Popular posts from this blog

Zargin Sace Wayar Madagwal Da Madam Korede Tayi/G Fresh Ya Musanta Maganar Bashi Da Lapiya

Wasu sirrikan mata guda 10 daya kamata ku sani wanda ba kowane namiji ne ya sansu ba