Zargin Sace Wayar Madagwal Da Madam Korede Tayi/G Fresh Ya Musanta Maganar Bashi Da Lapiya

Image
A Ranar Lahadi Babban Kaftin Na Nijeriya Ahmad Musa Ya Hada Wani Wasan Kwallon Kafar Na Manyan Sanannu A Arewa Domin Yin Zumunchi Inda Jaruma Da Manyan Celebrate Da Suka Hada Da Ali Nuhu, Umar M Sharif Madagwal ,Madam Korede Da Dai Sauransu Suka Halirchi Wajen PLAY ▶️ Saide A Yayin Da Aka Kammala Taron Ne Sai Wata Magana Ta Fito Ta Bakin Madagwal Inda Ya Bayyana Cewar Madam Korede Ta Sace Masa Waya A Yayin Da Suke Cin Abinchi Bayan Kammala Wasan Nasu Amma Nata Bangaren Madam Korede Ta Karya Batun Inda Ta Musanta Abun Har Abun Yakai Su Ga Zuwa Ofishin Yan Sanda Don Neman Hanginsa Da Yayi Kirarin Ta Tauye Masa Madagwal Ya Bayyana Hakane A Tattaunawa Sa Da  Freedom Radio Har Ya Bayyana Musu Yadda Abun Ya Faru Da Kuma Matsayar Kas Din Nasu Inda Yace Tun Fara Sun Sami Matsala Ne A Kwanakin Baya Da Madam Korede Inda Daga Bisani Ya Bashi Hakuri Har Allah Ya Kawo Wannan Taron Suka Hadu Da Ita Take Bibiyar PLAY ▶️ Yace A Lokacin Da Suka Kammala Wasan Shi Kuma Da Kaya...

Yadda Aka cafke wani mai makaranta da ya yi wa dalibarsa ‘yar shekara hudu fyade a bandaki

Wani mai makaranta dake zaman kanta a jihar Delta ya yi wa ‘yar shekara hudu fyade a makarantar sa.

Makarantar ‘Great Leaders International’ makaranta ne dake daukan yara kanana na raino sannan akwai fannin makarantar firamare da fannin sakandare duk a makarantar.

Mai makarantar Kuma Shugaban fannin sakandare Innocent Onwuegbule ya yi wa yarinyar fyade a wani bandaki dake makarantar inda a nan ya yi wa yarinyar allurar, ya yi amfani da almakashi ya farke gaban yarin sannan ya danne ta.
Gwamnishu ya ce zuwa yanzu Onwuegbule na tsare a ofishin ‘yan sanda dake Agbor.

A wani bidiyon da ya saka a shafinsa na Facebook Gwamnishu ya ce yarinyar ta dawo gida tana fitsarin jini a gida sannan da mahaifiyar ta duba ‘yarta ne ta gano ta’asar da aka aikata wa ‘yarta.

Ya ce Onwuegbule ya aikata haka ranar 4 ga Oktoba a kauyen Agbor dake karamar hukumar Ika ta Kudu.

A bidiyon mahaifiyar yarinyar ta ce mutane na kokarin tilasta ta wai a bata kudi ta tsuke bakinta amma ita dai ta ce tana son adalci.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Bright Edafe ya ce Onwuegbule ya aikata wannan ta’asa ne makonnin biyu da suka gabata kuma rundunar ‘yan sanda na gudanar da bincike akai har yanzu.
Edafe ya yi kira ga mutane da su guji karbar kudin daga hannun muggan mutane irin haka cewa yin haka na daga cikin matsalolin dake hana su gudanar da aikinsu yadda ya kamata.

Comments

Popular posts from this blog

Zargin Sace Wayar Madagwal Da Madam Korede Tayi/G Fresh Ya Musanta Maganar Bashi Da Lapiya

Wasu sirrikan mata guda 10 daya kamata ku sani wanda ba kowane namiji ne ya sansu ba