Zargin Sace Wayar Madagwal Da Madam Korede Tayi/G Fresh Ya Musanta Maganar Bashi Da Lapiya

Image
A Ranar Lahadi Babban Kaftin Na Nijeriya Ahmad Musa Ya Hada Wani Wasan Kwallon Kafar Na Manyan Sanannu A Arewa Domin Yin Zumunchi Inda Jaruma Da Manyan Celebrate Da Suka Hada Da Ali Nuhu, Umar M Sharif Madagwal ,Madam Korede Da Dai Sauransu Suka Halirchi Wajen PLAY ▶️ Saide A Yayin Da Aka Kammala Taron Ne Sai Wata Magana Ta Fito Ta Bakin Madagwal Inda Ya Bayyana Cewar Madam Korede Ta Sace Masa Waya A Yayin Da Suke Cin Abinchi Bayan Kammala Wasan Nasu Amma Nata Bangaren Madam Korede Ta Karya Batun Inda Ta Musanta Abun Har Abun Yakai Su Ga Zuwa Ofishin Yan Sanda Don Neman Hanginsa Da Yayi Kirarin Ta Tauye Masa Madagwal Ya Bayyana Hakane A Tattaunawa Sa Da  Freedom Radio Har Ya Bayyana Musu Yadda Abun Ya Faru Da Kuma Matsayar Kas Din Nasu Inda Yace Tun Fara Sun Sami Matsala Ne A Kwanakin Baya Da Madam Korede Inda Daga Bisani Ya Bashi Hakuri Har Allah Ya Kawo Wannan Taron Suka Hadu Da Ita Take Bibiyar PLAY ▶️ Yace A Lokacin Da Suka Kammala Wasan Shi Kuma Da Kaya...

Yan sanda sun kama mijin da ake zargi da kashe mata a Borno

A arewacin najeriya ana samun irin wannan labarun kashe mata ko kashe miji wanda a jihar borno kuma kashe mata da miji keyi wannan shine mummunan labari da ake samu majiyarmu ta samu wannan labari daga wani mutum mai amfani da kafar sada zumunta usman Rabi’u a shafinsa na facebook

Rundunar ‘yan sandan jihar Borno a ranar Juma’a ta tabbatar da kama wasu mutane biyu, Adamu Ibrahim da Bukar Wadiya bisa zargin kashe wata mata mai suna Fatima Alhaji-Bukar ‘yar shekara 24.
Marigayiyan mazauniyar Dikechiri ne a unguwar Bayan Gidan Dambe a cikin birnin Maiduguri a jihar Borno.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar yan sandan ysnkin, ASP Sani Kamilu, kuma ya bayyanawa manema labarai a Maiduguri ranar Juma’a.
A cewarsa, marigayiyan tana auren Mista Ibrahim, wanda shi ne babban wanda ake zargi da aikata laifin.

“A ranar 18 ga Oktoba, 2023, wani Adamu Alhaji Ibrahim mai unguwar Dikechiri bayan Gidan Dambe Maiduguri ya je sashin Gwange, tare da wani Bukar Wadiya, ya kai gawar wata mata da ya ce ita matarsa ce, ya kuma nemi agajin gaggawa daga jami’an tsaron ‘yan sanda,” in ji shi.

“Mijin wanda ya yi ikirarin cewa shi ma’aikaci ne a wani banki kasuwanci a Maiduguri, ya dawo daga aiki da misalin karfe 5:00 na yamma. sai ya iske marigayiyar tana kwance a cikin jini.”

A cewarsa, binciken farko da aka yi ya nuna cewa kafin faruwar lamarin, ma’auratan sun samu sabani a cikin gida kan zargin karin aure da mijin ya yi a gidan aurensu.

PLAY ▶️

Ya bayyana cewa an tsare gidan da lamarin ya faru kuma a yayin bincike an gano wasu kayayyaki da suka hada da gajeriyar fulawa guda daya, jaka, igiya, kafet jike da jini, wuka, da motar Honda da tabo

Malam Kamilu ya ce babu wata shaida da ta nuna cewa an karye kofa ko shiga gidan, kuma mijin ne kawai ke da mabudin gidan.
Ya ce mijin da Bukar Wadiya duk an kama su ne a matsayin wadanda ake tuhuma, yana mai cewa ana ci gaba da gudanar da bincike mai zurfi domin gurfanar da su gaban kuliya.

Comments

Popular posts from this blog

Zargin Sace Wayar Madagwal Da Madam Korede Tayi/G Fresh Ya Musanta Maganar Bashi Da Lapiya

Wasu sirrikan mata guda 10 daya kamata ku sani wanda ba kowane namiji ne ya sansu ba