Zargin Sace Wayar Madagwal Da Madam Korede Tayi/G Fresh Ya Musanta Maganar Bashi Da Lapiya

Image
A Ranar Lahadi Babban Kaftin Na Nijeriya Ahmad Musa Ya Hada Wani Wasan Kwallon Kafar Na Manyan Sanannu A Arewa Domin Yin Zumunchi Inda Jaruma Da Manyan Celebrate Da Suka Hada Da Ali Nuhu, Umar M Sharif Madagwal ,Madam Korede Da Dai Sauransu Suka Halirchi Wajen PLAY ▶️ Saide A Yayin Da Aka Kammala Taron Ne Sai Wata Magana Ta Fito Ta Bakin Madagwal Inda Ya Bayyana Cewar Madam Korede Ta Sace Masa Waya A Yayin Da Suke Cin Abinchi Bayan Kammala Wasan Nasu Amma Nata Bangaren Madam Korede Ta Karya Batun Inda Ta Musanta Abun Har Abun Yakai Su Ga Zuwa Ofishin Yan Sanda Don Neman Hanginsa Da Yayi Kirarin Ta Tauye Masa Madagwal Ya Bayyana Hakane A Tattaunawa Sa Da  Freedom Radio Har Ya Bayyana Musu Yadda Abun Ya Faru Da Kuma Matsayar Kas Din Nasu Inda Yace Tun Fara Sun Sami Matsala Ne A Kwanakin Baya Da Madam Korede Inda Daga Bisani Ya Bashi Hakuri Har Allah Ya Kawo Wannan Taron Suka Hadu Da Ita Take Bibiyar PLAY ▶️ Yace A Lokacin Da Suka Kammala Wasan Shi Kuma Da Kaya...

Hukuncin Kotu 5 da Su ka Girgiza Kowa a Shari’ar Zaben Gwamnoni da ‘Yan Majalisa

Abuja - Bayan an ayyana wadanda su ka yi nasara a zaben 2023, kotu suna cigaba da yanke hukuncin kararrakin da aka gabatar masu. 

Kamar yadda lauyan Abba Kabir Yusuf ya fada, wannan ne karon farko da za a rusa nasarar zabe saboda rashin hatimi, sa hannu da kwanan wata. 

A dalilin haka aka sokewa NNPP kuri’u fiye 165, 000, kotun korafin zabe ta ce Nasiru Yusuf Gawuna ne halattaccen wanda ya ci zaben gwamnan Kano 

Da aka je kotu Natasha Akpoti-Uduaghan ta yi nasarar karbe kujerar Sanata mai wakiltar Kogi ta tsakiya a majalisar dattawa a hannun jam’iyyar APC. 

Abin da ya fi daukar hankali shi ne ganin Natasha Akpoti-Uduaghan mace ce da ta yi nasara a karkashin PDP a mazabar da Gwamna Yahaya Bello ya fito. 
BBC ta ce babban abin da aka fi damuwa da shi yanzu shi ne matakin da Simon Lalong zai dauka da kotu ta ce Ministan ne Sanatan Filato ta kudu. 

Sauran shari’o’in zaben jihar Filato sun bada mamaki ganin yadda jam’iyyar PDP ta rasa kujeru bakwai a majalisa, mukamanta sun koma hannun APC da LP. 

Sanata Elisha Abbo ya fuskanci kalubale iri-iri a zaben Sanatan Adamawa ta Arewa, sai a kotun ɗaukaka ƙara da ke zama a Abuja, aka kawo karshensa a 2023. 

Babban kotun ta ce Rabaren Amos Yohanna ne wanda ya ke da rinjayen halatattun ƙuri'u. hakan ya kawo karshen Sanatan da ya yi suna a majalisar dattawa. 

Ana da labarin yadda kotu soke nasarar Sanata Darlington Nwokocha (LP), ta ce Kanal Austin Akobundu (PDP) ne Sanatan Abia ta tsakiya a majalisa.

Sai dai zanga-zanga ta barke saboda magoya bayan LP ba su ji dadin hukuncin ba, an ji PDP ta na cewa an bi ta bayan fage a dawo da Sanatan da aka sauke.

 

Comments

Popular posts from this blog

Zargin Sace Wayar Madagwal Da Madam Korede Tayi/G Fresh Ya Musanta Maganar Bashi Da Lapiya

Wasu sirrikan mata guda 10 daya kamata ku sani wanda ba kowane namiji ne ya sansu ba