Zargin Sace Wayar Madagwal Da Madam Korede Tayi/G Fresh Ya Musanta Maganar Bashi Da Lapiya

Image
A Ranar Lahadi Babban Kaftin Na Nijeriya Ahmad Musa Ya Hada Wani Wasan Kwallon Kafar Na Manyan Sanannu A Arewa Domin Yin Zumunchi Inda Jaruma Da Manyan Celebrate Da Suka Hada Da Ali Nuhu, Umar M Sharif Madagwal ,Madam Korede Da Dai Sauransu Suka Halirchi Wajen PLAY ▶️ Saide A Yayin Da Aka Kammala Taron Ne Sai Wata Magana Ta Fito Ta Bakin Madagwal Inda Ya Bayyana Cewar Madam Korede Ta Sace Masa Waya A Yayin Da Suke Cin Abinchi Bayan Kammala Wasan Nasu Amma Nata Bangaren Madam Korede Ta Karya Batun Inda Ta Musanta Abun Har Abun Yakai Su Ga Zuwa Ofishin Yan Sanda Don Neman Hanginsa Da Yayi Kirarin Ta Tauye Masa Madagwal Ya Bayyana Hakane A Tattaunawa Sa Da  Freedom Radio Har Ya Bayyana Musu Yadda Abun Ya Faru Da Kuma Matsayar Kas Din Nasu Inda Yace Tun Fara Sun Sami Matsala Ne A Kwanakin Baya Da Madam Korede Inda Daga Bisani Ya Bashi Hakuri Har Allah Ya Kawo Wannan Taron Suka Hadu Da Ita Take Bibiyar PLAY ▶️ Yace A Lokacin Da Suka Kammala Wasan Shi Kuma Da Kaya...

Wani ya maka asibiti a kotu bisa zargin lalata masa ƴaƴan maraina a Abuja

Wani matashi dan shekara 11, Nelson George, ya shigar da kara ta Naira miliyan 100m a kan asibitin Limi Children’s Hospital Limited bisa zargin rashin ƙwarewa da ya kai ga lalacewar ɗan marainan sa.

Nelson, wanda ya shigar da karar ta hannun mahaifinsa, Bankole George, ya kuma roki mai shari’a Akanbi Yusuf na babbar kotun tarayya da ke Kubwa, da ya ba da umarnin cewa asibitin ya biya shi kudi naira miliyan 5 a matsayin kudin shigar da karar.

A cikin karar mai lamba: FCT/HC/CV/7356/2023 mai kwanan 28 ga watan Agusta ta hannun lauyansa, Emmanuel Ekpenyong na Fred-Young & Evans LP, Nelson ya kara da rokon kotun da ta baiwa asibitin umarnin su bashi hakuri a rubuce a bisa ta’asar da aka yi masa.

Mai shigar da ƙarar ya kuma hada da wasu ƙungiyoyin kiwon lafiya guda hudu a matsayin waɗanda ake kara na 2 zuwa 4 a shari’ar.

Haka kuma ya bukaci kotun da ta bayyana cewa ya kamata wadanda ake kara na 2 zuwa na 4 su kara kaimi wajen ganin sun gudanar da ayyukansu a karkashin ikonsu kamar yadda dokokin da suka kafa su ke ba da kariya da inganta muradunsa da jin dadinsa, ciki har da na ‘yan uwa al’ummar Najeriya.

A cikin sanarwar da ya bayar ta hadin gwiwa, Nelson ya ce yana da shekaru 11 a halin yanzu “a karamar Sakandare aji 3 kuma yana zaune a karkashin iyayensa, Bankole George wanda shine mai kula da shi.”
Har yanzu wadanda ake tuhumar ba su amsa kiran kotun ba har zuwa lokacin wannan rahoton.

Mai shari’a Yusuf ya sanya ranar 20 ga watan Disamba domin sauraron karar.

Comments

Popular posts from this blog

Zargin Sace Wayar Madagwal Da Madam Korede Tayi/G Fresh Ya Musanta Maganar Bashi Da Lapiya

Wasu sirrikan mata guda 10 daya kamata ku sani wanda ba kowane namiji ne ya sansu ba