Zargin Sace Wayar Madagwal Da Madam Korede Tayi/G Fresh Ya Musanta Maganar Bashi Da Lapiya

Image
A Ranar Lahadi Babban Kaftin Na Nijeriya Ahmad Musa Ya Hada Wani Wasan Kwallon Kafar Na Manyan Sanannu A Arewa Domin Yin Zumunchi Inda Jaruma Da Manyan Celebrate Da Suka Hada Da Ali Nuhu, Umar M Sharif Madagwal ,Madam Korede Da Dai Sauransu Suka Halirchi Wajen PLAY ▶️ Saide A Yayin Da Aka Kammala Taron Ne Sai Wata Magana Ta Fito Ta Bakin Madagwal Inda Ya Bayyana Cewar Madam Korede Ta Sace Masa Waya A Yayin Da Suke Cin Abinchi Bayan Kammala Wasan Nasu Amma Nata Bangaren Madam Korede Ta Karya Batun Inda Ta Musanta Abun Har Abun Yakai Su Ga Zuwa Ofishin Yan Sanda Don Neman Hanginsa Da Yayi Kirarin Ta Tauye Masa Madagwal Ya Bayyana Hakane A Tattaunawa Sa Da  Freedom Radio Har Ya Bayyana Musu Yadda Abun Ya Faru Da Kuma Matsayar Kas Din Nasu Inda Yace Tun Fara Sun Sami Matsala Ne A Kwanakin Baya Da Madam Korede Inda Daga Bisani Ya Bashi Hakuri Har Allah Ya Kawo Wannan Taron Suka Hadu Da Ita Take Bibiyar PLAY ▶️ Yace A Lokacin Da Suka Kammala Wasan Shi Kuma Da Kaya...

Yadda ta kaya a taron Hisbah da ‘yan Tiktok a Jihar Kano

Hukumar Hisbah a Jihar Kano da ke arewacin Nijeriya ta yi wa ƴan Tiktok alkawari da busharar cewa za a yi musu auren gata da ba su sana’o’i da tura su ƙaro karatu, idan har suka sauya halayensu da kuma daina yaɗa abubuwan da ba su dace ba a shafukansu.

Kwamandan rundunar Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa da mataimakansa biyu ne suka sanar da hakan a wata ganawa ta musamman da suka yi da ƴan Tiktok ɗin a oifshin hukumar da ke birnin Kano a ranar Litinin da marece.

An yi wannan taro ne kwanaki kadan bayan wani gagarumin samame da Hisbah ta dinga yi a wasu wuraren taruwar jama’a a birnin Kano, inda ta kama matasa maza da mata da dama, lamarin da ya jawo ce-ce-ku-ce sosai.

An ga fitattun ƴan Tiktok irin su Murja Ibrahim Kunya a wurin.

“Daga cikin ayyukan Hisbah har da gyaran tarbiyya don mu dinga bai wa matasa shawarar yadda za su tafiyar da rayuwarsu cikin kamala ba tare da lalata samartakar su ba ta yadda za su yi nadama a nan gaba,” a cewar Sheikh Daurawa.

Ya ƙara da cewa ganin yadda mutane suke amfani da shafin Tiktok barkatai ya sa hukumar ta ga bai kamata ta bar abubuwa na taɓarɓarewa ba.

“Mun gayyace ku a matsayinku na matasa don bai wa Hisbah gudunmawa kan yadda za a daƙile irin ayyuka marasa kyau da ɓata tarbiyya ba.

“Mun lura wasu kan yi kasuwanci ko fadakarwa ko koyar da karatun Kur’ani ko na zamani ko koyar da zaman aure da ma sana’o’i. Wasu kuma abin da suke yi bai dace ba. Akwai takaici a ce kun ɓata rayuwar ƙuruciyarku a kan hakan,” Malam ya shaida wa 'yan Tiktok ɗin.

Sheikh Daurawa ya ba da misali da yadda duk abin da aka dora a intanet ba ya taɓa gogewa inda nan da wasu shekaru za su iya zame wa mutum aikin nadama.

Ya nanata muhimmancin ƴan Tiktok din da irin gudunmawar da haɗin kai tsakaninsu da Hisbah za ta kawo gyaran tarbiyya.

“Ba za mu iya gyaran nan ba sai da hannunku, idan kuka yi fada ku yi ta zage-zage a junanku marasa dadin ji, abin ba ya mana dadi.

“Tiktok ta zama alheri ya wani waje, ta wani wajen kuma ya zama sharri. Ko Amurka da China mun san yadda a yanzu al’amarin Tiktok ya sha musu kai,” in ji Malam.
Malam ya jaddada buƙatar Hisbah ta neman gudunmawar ƴan Tiktok don tsarkake al’umma a aikin da take yi mai take “Operation Kawar da Badala.”

Comments

Popular posts from this blog

Zargin Sace Wayar Madagwal Da Madam Korede Tayi/G Fresh Ya Musanta Maganar Bashi Da Lapiya

Wasu sirrikan mata guda 10 daya kamata ku sani wanda ba kowane namiji ne ya sansu ba