Zargin Sace Wayar Madagwal Da Madam Korede Tayi/G Fresh Ya Musanta Maganar Bashi Da Lapiya

Image
A Ranar Lahadi Babban Kaftin Na Nijeriya Ahmad Musa Ya Hada Wani Wasan Kwallon Kafar Na Manyan Sanannu A Arewa Domin Yin Zumunchi Inda Jaruma Da Manyan Celebrate Da Suka Hada Da Ali Nuhu, Umar M Sharif Madagwal ,Madam Korede Da Dai Sauransu Suka Halirchi Wajen PLAY ▶️ Saide A Yayin Da Aka Kammala Taron Ne Sai Wata Magana Ta Fito Ta Bakin Madagwal Inda Ya Bayyana Cewar Madam Korede Ta Sace Masa Waya A Yayin Da Suke Cin Abinchi Bayan Kammala Wasan Nasu Amma Nata Bangaren Madam Korede Ta Karya Batun Inda Ta Musanta Abun Har Abun Yakai Su Ga Zuwa Ofishin Yan Sanda Don Neman Hanginsa Da Yayi Kirarin Ta Tauye Masa Madagwal Ya Bayyana Hakane A Tattaunawa Sa Da  Freedom Radio Har Ya Bayyana Musu Yadda Abun Ya Faru Da Kuma Matsayar Kas Din Nasu Inda Yace Tun Fara Sun Sami Matsala Ne A Kwanakin Baya Da Madam Korede Inda Daga Bisani Ya Bashi Hakuri Har Allah Ya Kawo Wannan Taron Suka Hadu Da Ita Take Bibiyar PLAY ▶️ Yace A Lokacin Da Suka Kammala Wasan Shi Kuma Da Kaya...

Ƴan bindiga sun kai wani ƙazamin hari wanda yayi sanadiyar rasuwar rayuka da yawa a kastina

Wasu ƴan bindiga ɗauke da makamai sun kashe Mai gari da ɗansa da wasu mutune taƙwas a kauyen Kukar Babangida da ke Karamar Hukumar Jibia a Jihar Katsina.

Kamar yadda Katsina Reporters ta samu, a daren ranar Laraba ne ’yan bindigar suka yi wa mutanen ki-san gilla, ciki har wani mai gadi da suka yi wa yan-kan rago.

Wani dan yankin da ya nemi a boye sunansa ya ce, zugar ’yan bindigar sun kai harin ne da misalin karfe 10 na dare, inda “suka ka-she mai gari Magaji Haruna da dansa Idris, tare da wasu mutane uku a gidansa.

Sun kuma shiga wani kamfani mai suna Tinna Tech inda suka yi wa wani mai gadi yan-kan rago, dayan kuma suka harbe shi har lahira, sannan suka cinna wa manyan motoci biyu da wata karama wuta.”

Wani mazaunin yankin ya ce maharan sun yi awon gaba da mata dama, amma ba a kai ga tantance adadinsu ba, kamar yadda Aminiya suka ruwaito.

Shaidan ya ce tun da misalin karfe 5 na yammacin ranar aka fara fargabar yiwuwar kawo hari, sakamakon ganin ’yan ta’adda a kusa da kauyukna Taka-Tsaba da Yargeza.

Ya ce, saboda haka aka sanar da jami’an tsaro abin da ke faruwa, amma kuma a karshe da ’yan bindigar suka kawo farmakin babu wani mataki da suka dauka na dakile harin.
“Duk da cewa jami’an tsaro sun ba mu tabbacin cewa akwai karin jami’ai da za su turo idan har akwai barazanar hari, amma haka ’yan bindigar suka zo suka shafe sa’o’i suna cin karensu babu babbaka, jami’an tsaro sun zo ba.

“Sai da ’yan bindigar suka gama barnarsu suka tafi sannan wata motar jami’an tsaro kwaya daya ta zo,” in ji shi.

Mazauna yankunan dai na zargin gaggan jagororin ’yan ta’adda Dankarami da Dangote ne ke aiwatar da hare-haren da ake fama da su a Karamar Hukumar Jibia da kewaye.

Comments

Popular posts from this blog

Zargin Sace Wayar Madagwal Da Madam Korede Tayi/G Fresh Ya Musanta Maganar Bashi Da Lapiya

Wasu sirrikan mata guda 10 daya kamata ku sani wanda ba kowane namiji ne ya sansu ba